Isa ga babban shafi
Lebanon

Hezbollah ta ce ba ta tsora hari daga Amurka ko Saudiyya

Kungiyar Hezbollah ta kasar Lebanon ta ce ko gezau ba ta yi ba dangane da barazanar Amurka da Saudiyya na kai ma ta hari da kuma kakaba ma ta takunkumai, kwanaki bayan shugaba Donald Trump ya soke ta tare da kasar Iran.

Shugaban Hezbollah, Hassan Nasrallah yana jawabi a kudancin Beyrouth ranar  24 ga watan oktoban 2015.
Shugaban Hezbollah, Hassan Nasrallah yana jawabi a kudancin Beyrouth ranar 24 ga watan oktoban 2015. AFP PHOTO / ANWAR AMRO
Talla

Shuagban kungiyar Hassan Nasrallah ya ce Hezbollah ba ta tsoron yaki da takunkumi ko kuma farfagandar kafofin yada labarai.

Nasrallah ya ce barazanar kisa ba ta dauke musu hankali, kamar dai yadda ya bayyana a sakon da ya aikewa magoya bayan sa dangane da cika shekaru 17 da janyewar Isra’ila daga kudancin Lebanon.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.