Philippines
Abun fashewa ya raunata masu bikin krismeti 16
Akalla mutane goma sha shida ne suka sami rauni bayan fashewa wasu abubuwa a yayin da mabiya addinin krista ke gudanar da addu’oi na shigowar Krismeti a garin Mindanao da ke wani tsibiri a kudancin kasar Phillipines.
Wallafawa ranar:
Talla
Sanarwar da ‘yan sandan kasar suka fitar na cewa al’ummar da ke gudanar da addu’oin sun fada cikin rudani bayan fashewar da aka samu.
Ana ci gaba da gudanar da bincike yayin da jam’ian tsaro ke cewa sun yi nasarar kwance wasu bama-bamai da aka ajiye a daf da wurin da al’amarin ya auku a yau asabar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu