Majalisar Dinkin Duniya ta soki shirin Isra'ila kan yankin Falasdinawa
Majalisar Dinkin Duniya tace yunkurin kasar Isra’ila na halarta gina gidaje 4,000 a yankunan Falasdinawa dake gabar yamma da kogin Jordan haramtacce ne, domin ya sabawa dokokin duniya.
Wallafawa ranar:
Babban jami'i na ofishin kare hakkin Bil Adama na Majalisar, Zeid Ra’ad ya bukaci Majalisar Israila ta sake tunani akan matakin wanda yace zai bata sunanta a idanun duniya.
Yanzu haka Yahudawa 400,000 ke zama a gabar yamma da Kogin Jordan wanda yanki ne na Falasdinawa.
Majalisar Dinkin Duniya, Amurka da kuma Tarayyar Turai duk sun bayyana matakin a matsayin yunkurin soke shirin kafa kasar Falasdinu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu