Tarzoma ta barke tsakanin Palasdinawa da Jami'an Isra'ila
Rikici ya barke tsakanin Palasdinawa da Sojojin Isra’ila a birnin Hebron da ke yankin yamma da Kogin Jordan, a yayin da Palasdinawan suka yi jana’izar ‘yan uwansu matasa biyar da suka rasa rayukansu a arangama da Jami’an tsaron na Isra’ila.
Wallafawa ranar:
Wanann dai na zuwa ne bayan jami’an Isra’ila da ke kula da kan iyaka sun bindige wani Bafalasdine har lahira a wajen binciken ababan hawa, inda suka ce ya yi yunkurin daba wa daya daga cikinsu wuka.
Tun bayan da tarzomar ta fara a watan jiya a birnin Kudus, kawo yanzu Palasdinawa 66 sun rasa rayukansu, inda Yahudawa suka rasa mutane tara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu