Isa ga babban shafi
Yemen

Fada ya sake barkewa a Yemen bayan tsagaita wuta

Fada ya sake barkewa a Yemen duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da ta soma aiki a yau Assabar inda Rahotanni suka ce ‘Yan tawaye sun gwabza fada da dakarun gwamnati a garin Taez da ke kudu maso yammacin kasar.

Sama da mutane 7,000 suka mutu a rikicin Yemen
Sama da mutane 7,000 suka mutu a rikicin Yemen REUTERS/Anees Mahyoub
Talla

Majiyoyin tsaro da na lafiya sun ce ‘Yan tawayen Huthi sun harba makamin roka inda fararen hula uku suka mutu yayin da kuma aka kashe ‘Yan tawaye hudu a wani fada da suka gwabza da dakarun gwamnati kusa da garin na Taez.

Amurka ce dai ta jagoranci amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta ta sa’o’I 48 da nufin bude kofar hawa teburin sulhu domin kawo karshen rikicin kasar da ya lakume rayukan dubban mutane.

Saudiya da kawayenta da ke taimakawa dakarun gwamnatin Yemen akan ‘Yan tawayen Huthi ‘Yan Shi’a ne suka sanar da amincewa da yarjejeniyar wacce kuma rahotanni suka ce ta soma aiki da safiyar Assabar.

An dai dade bangaren gwamnatin Yemen da Saudiya ke mara baya na yin watsi da yarjejeniyar tsagaita wutar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.