Isa ga babban shafi
Afghanistan

IS ta kashe mutane 80 a harin da ta kai a Kabul

Kungiyar IS da ke da’awar jihadi ta ce ita ta kai hare haren bama bamai guda biyu akan gangamin masu zanga-zanga a birnin Kabul na Afghanistan inda mutane sama da 80 suka mutu sannan sama da 200 suka jikkata.

Kungiyar ISIL ta dauki alhakin kashe mutane sama da 80 a harin Kabul
Kungiyar ISIL ta dauki alhakin kashe mutane sama da 80 a harin Kabul REUTERS/Mohammad Ismail
Talla

Ma’aikatar cikin gida ta ce adadin mutanen da suka mutu na iya karuwa bayan tabbatar da mutuwar mutane 80.

An dai kai harin ne akan mabiya Shi’a a dandalin Deh Mazang a Kabul wadanda ke zanga-zangar adawa da dauke hanyar lantarki zuwa yankinsu.

Kungiyar Taliban ta nisanta kanta da harin tare da yin allawadai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.