Afghanistan
IS ta kashe mutane 80 a harin da ta kai a Kabul
Kungiyar IS da ke da’awar jihadi ta ce ita ta kai hare haren bama bamai guda biyu akan gangamin masu zanga-zanga a birnin Kabul na Afghanistan inda mutane sama da 80 suka mutu sannan sama da 200 suka jikkata.
Wallafawa ranar:
Talla
Ma’aikatar cikin gida ta ce adadin mutanen da suka mutu na iya karuwa bayan tabbatar da mutuwar mutane 80.
An dai kai harin ne akan mabiya Shi’a a dandalin Deh Mazang a Kabul wadanda ke zanga-zangar adawa da dauke hanyar lantarki zuwa yankinsu.
Kungiyar Taliban ta nisanta kanta da harin tare da yin allawadai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu