Yan adawar kasar Syria sun kasa fitar da wakilan da zasu halarcesu a taronsu da Gwamnati
Hare haren jiragen yakin Rasha ya hallaka fararen 90 a yankin gabashin kasar Syriya, ana sauran yan kwanaki a buda taron tattauna neman zaman lafiya a kasar a birnin Janiva
Wallafawa ranar:
A gobe litanin ne ya kamata a ce an fara taron, sai dai yan adawa basu kammala shirya kansu ba domin sanin wadanda zasu wakilcesu a taron, al’amarin da ya sa ake ganin sai an matsar da shi gaba da wasu yan kwanaki a cewar MDD
A dai gefen kuma a kalla mutane 47 da suka hada da yara 9 da mata biyu ne aka kashe a cikin hare-haren da jiragen saman kasar Rasha suka kai a gabashin kasar ta Syriya, inda a jiya harin yayi sanadiyar mutuwar mutane 44 a cewar kungiyar kare hakkin dan adam ta OSDH
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu