Isa ga babban shafi
Saudiya

Saudiya ta kulla kawance da kasashe 34 kan yaki da ta’addanci

Kasar Saudiyya ta kafa rundunar hadin guiwa da ta kunshi kasashe 34 domin yakar ta’adanci da ake fakewa da jihadi ana salwantar da rayukan jama’a.

Ministan tsaron Saudiya Yarima Mohammed bin Salman
Ministan tsaron Saudiya Yarima Mohammed bin Salman REUTERS
Talla

Kasashen da Saudiya ta kulla kawancen da su sun hada da  Masar da Turkiya da wasu kasashen a gabas ta tsakiya da Asiya da Afrika.

Amma babu Iran cikin kasashen da Saudiya ta kulla kawancen da su kan yakar Ta’addanci.

Ministan Tsaro na Saudiyya Yarima Mohammed Bin Salman Al-Saud ya ce  kawancen kasashen zai tunkari matsalolin kasashen musulmi da ta’addanci.

Sannan za su hada kai da sauran kasashe da ke yaki da ta’adanci a duniya.

Saudiya tace kasashen za su yaki ta’addanci a ko ina a duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.