Taliban ta kashe mutane 5 a Kabul
Jami’an tsaron Afghanistan sun yi nasarar murkushe mayakan Taliban da suka kaddamar da hare hare a kusa da ofishin jekadancin kasashen waje a Kabul, kamar yadda Ministan cikin gida Sediq Sediqqi ya sanar a shafin shi na Twitter.
Wallafawa ranar:
Akalla mutune biyar aka kashe a hare haren da mayakan Taliban sun kai yau Assabar a kusa da ginin ofishin jekadancin kasar Spain a Kabul. Akwai ‘Yan sanda 4 cikin wadanda suka mutu.
An shafe sa’o’I jami’an tsaron Afghanistan na musayar albarussai da ‘Yan Taliban.
Wannan kuma na zuwa ne sa’o’I bayan shugaban Afghanistan Ashraf Gani ya bayyana kwarin guiwarsa na komawa teburin tattaunawa da Taliban nan da makwanni biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu