Isra'ila za ta killace Falasdinawa a birnin Kudus
Majalisar tsaron kasar Isra’ila ta bada umurnin killace yankin da Falasdinawa suke zama a cikin birnin Kudus dan dakile tashin hankalin da ake ci gaba da samu dake da nasaba da harin da ake kai wa da wukake.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Ofishin Firaministan kasar Benjamin Netanyahu ya ce majlaisar ta dauki matakai da dama da suka hada da killace yankin da kuma murkushe duk wanda aka samu dauke da makami.
Akalla Yahudawa 7 aka kashe a tashe tashen hankulan na baya bayan nan, yayin da jami’an tsaron Isra’ila suka kashe Falasdinawa 30.
Sakatare Janar na Majalisar dinkin duniya, Ban Ki-Moon ya bukaci Isra’ila da ta sake nazari sosai kan yadda Jami’anta ke amfani da karfin da ya wuce kima a fafatawa da Falasdinawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu