Jami'an Isra'ila sun kashe Falasdinawa
Akalla Falasdinawa shida sun rasa rayukansu yayinda da dama suka jikkata bayan dakarun Isra’ila sun bude musu wuta a lokacin da Falasdinawan ke zanga zanga a kan iyakar yankin zirin Gaza.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Wani shaidan gani da ido mai suna Ezz Zanoun ya ce , Jami’an tsaron na yawaita harbe harben bindiga akan iyakar, amma na yau ya wuce misali.
Cikin wadanda suka rasa rayukansu, akwai yaro mai shekaru 15 da Jamian suka bindige har lahira kuma akalla mutane 10 cikin mutane 70 da suka jikkata na cikin mawuyacin hali kamar yadda wata majiyar kiwon lafiya ta sanar.
A lokacin da ya ke gabatar da huDuba a yau jumma’a, shugaban Hamas, Isma’il Haniyeh ya yi kira ga al-ummar Falasdinawa da su kara kaimi wajen arangama da dakarun Isra’ila a yankin yamma da kogin Jordan da kuma gabashin birnin kudus.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu