Isa ga babban shafi
Iraqi

Sakacin Jami’an gwamnati ya baiwa ISIL nasara iko da Mosul

Wani bincike ya nuna cewa sakacin manyan jami’an gwamnati Iraqi ne yasa mayakan ISIL suka iya kwace birnin Mosul a bara, ganin yadda suka nuna halin ko in kula bayan sun samu mahinman rahotanni da ke gargadin cewa mayakan na kokarin kai hare hare a cikin kasar.

REUTERS/Hadi Mizban/Pool
Talla

Rahotan ya bayyana sunan manyan jami’an gwamnati da cikin su har da mataimakin shugaban kasar Nuri al-Maliki da ke da hannu a nuna halin ko in kula akan tsaron kasar.

Rahotan ya kara da cewa duk manyan jami’an gwamnatin na sane mayakan ISIL na shirin kai hare hare a cikin kasar kuma sun gagara daukar matakai har sai dai mayakan suka yi nasarar kwace babban birnin na Mosul.

Sakamakon hakan ne dakarun gwamnati suka tafka kura-kurai a yayin fafatawar su da mayakan har suka kai ga nasarar karbe birnin.

Rahotan dai ya zargi al-Maliki da kasa kafa runduna soji mai karfi da ka iya fuskantar duk wata yan ta’ada a kasar bayan karbe birnin Mosul da yankin Nineveh, yanzu mayakan sun nufi kudancin kasar da niyar karbe ikon yankin baki daya.

Tuni dai mataimakin shugaban kasar Nurul al-Maliki ya yi watsi da wannan rahoton inda ya ce bashi da wani amfani.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.