Isa ga babban shafi
Afghanistan

Afghanistan ta koma teburin sulhu da Taliban

Tawagar Gwamnatin kasar Afghanistan ta soma zaman tattaunawa da Mayakan Taliban a Pakistan da nufin samun jituwa don kawo karshen rikicin Mayakan na tsawon shekaru 13.

Mayakan Taliban sun shafe shekaru 13 suna yaki a Afghanistan
Mayakan Taliban sun shafe shekaru 13 suna yaki a Afghanistan AFP PHOTO / Noorullah Shirzada
Talla

Ma’aikatar harakokin wajen Pakistan ta fadi a cikin wata sanarwa cewa Tawagar Afghanistan sun gana da wakilan Taliban a garin Murree da ke arewacin Islamabad.

Sanarwar tace bangarorin biyu sun tattauna matakan da ya kamata a dauka domin tabbatar da zaman lafiya a Afghanistan. Sanarwar kuma ta kara da cewa bangarorin biyu sun amince su sake tattaunawa idan an idar da Azumin watan Ramadan.

Mai Magana da yawun shugaban kasar Sayed Zafar Hashemi ya ce tawagar gwamnatin na karkashin mataimakin ministan harkokin wajen kasar ne Hekmat Khalil Karzai.

Kungiyar Taliban ba ta fito fili ta bayyana shirin shiga taron ba, amma daya daga cikin shugabanin ta ya ce sun tafi kasar Pakistan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.