Isra'ila-Falesdinawa
Isra'ila ta soki Amurka game da goyon bayan gwamnatin Palasdinu
Ministoci da dama a Isra’ila sun soki Amurka bayan da ta goyi bayan sabuwar gwamnatin hada-ka da aka kafa tsakanin Hamas da Fatah a Palasdinu.
Wallafawa ranar:
Talla
Ministan yada labaran Isra’ila Gilad Erdan, ya ce abin da Amurka ta yi babban kuskure ne, domin kuwa ba ta yadda za a goyi bayan gwamnatin da ke kunshe da ‘yan Hamas wadanda a cewarsa su ne ke kashe ‘yayan Yahudawa.
A shekaranjiya ne dai Amurka ta bayyana cewa a shirye take domin yin aiki da gwamnatin da aka kafa a Palasdinu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu