Isa ga babban shafi
Isra'ila-Falesdinawa

Isra'ila na cin zarafin fararen Hula inji Amaruka

Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta bayyana Isra’ila  a matsayin kasar dake taka gagarumar rawa wajen fada da ayyukan ta’addanci a Duniya, To sai dai rahoton na bana ya bayyana cewa Israel ta aikata ayyuka na asha har guda 399, wadanda ake iya fassarawa a matsayin ta’addanci.Rahoton ya bayar da misali da abinda masu tsatsauran ra’ayin yahudancin a Isra’ila ke aikatawa da suka hada da kai hare-hare kan fararen hula, da lalata kadarorinsu, sannan kuma da rusa masallatai har ma da mujami’u ko dai a yankin Palasdinawa na yammacin kogin Jordan ko kuma a birnin Quds. 

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu tare da  Jonh Kerry na kasar Amaruka
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu tare da Jonh Kerry na kasar Amaruka REUTERS/Jacquelyn Martin/Pool
Talla

Duk da yake hukumomin Tel Aviv sun kafa runduna ta musamman domin bincike da kuma yiyuwar hukunta wadanda ke aikata irin wadannan laifufuka, to amma hakan bai wadatar ba a cewar rahoton, kuma dole a kira wannan ta’asa a matsayin ta’addanci.
Tuni dai rundunar ‘yan sandan Isra’ila ta mayar da martani dangane da wannan zargi, inda mai magana da yawunta Michy Rosenfeld ke cewa ba ta yadda za a danganta wadannan hare-hare da yahudawan ke kai wa Falasdinawa a matsayin ta’addanci.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.