Amurka ta ja kunnen kasar Isra'ila
Kasashen Isra’ila da Falesdinu sun nuna aniyar su na hadiye fushin su, a dai- dai lokacin da ake shirin komawa tattaunawar neman zaman lafiya tsakanin kasashen biyu a karkashin jagorancin kasar Amurka.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Ya dace Isra’ila ta gujewa abinda zai sa a dangantata da kasar mai nuna wariya ga larabawa.
A ranar lahadi da ta gabata ne Manzon kasar Amaruka Martin Indyk ya koma birnin washington domin tataunawa bayan da gwamnatin firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahou ya dakatar da tataunawar da suke yi da Falesdinawa .
A yayin da falasdinawa suka yi amfani da wannan dakatar da tattaunawar da Isra’ila ta yi wanda ya kai su ga cimma yarjejeniyar hadin kai tsakanin kungiyar PLO ta shugaba Mahmud Abbas da Hamas mai mulkin zirin gaza, kungiyar da bata yarda da kasancewar Isra’ila a matsayin kasa intaciyar ba.
Yarjejeniyar da suka cimma dai ta tanadi kafa gwamnatin rikon kwarya ta masalaha da zata hada manyan mutanen da basu da bangare a Falesdinu .
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu