Isa ga babban shafi
Thailand

Kotu ta haramta zaben Thailand

Kotun duba tsarin mulki a kasar Thailand ta haramta zaben kasar da aka gudanar watan jiya, bayan an kwashe makwanni ‘yan adawa na zanga-zanga a fadin kasar. Kotun tace zaben ya sabawa kundin tsarin mulki saboda akwai yankunan da ba a gudanar da zaben ba.

Masu zanga-zanga a kasar Thailand
Masu zanga-zanga a kasar Thailand REUTERS
Talla

‘Yan adawa dai sun kauracewa zaben sannan masu zanga-zangar kin jinin gwamnatin Yingluck Shinawatra suka hana a gudanar da zaben a wasu runfunan zabe.

Zuwa yanzu babu wata rana da aka kebe domin gudanar da sabon zabe a kasar Thailand da ke fama da rikicin siyasa tun a watan Nuwamban bara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.