Isa ga babban shafi
Indonesia

Dutsi mai amon wuta ya yi ta’adi a Indonesia

Mutane biyu ne aka ruwaito sun mutu a ƙasar Indonesia bayan da Dutsi mai amon wuta ya turmuƙe da hayaƙi tare da yin watsi da duwatsu da suka abkwa gidajen mutane a yankin Java. Rahotanni sun ce wasu mutane ne ƴan shekaru 60 guda biyu suka mutu a yankin Malang da ke lardin tsibirin Java.

Runfunan gidajen mutane lullube da tokar amon wuta daga dutsin Kelud a Indonesia
Runfunan gidajen mutane lullube da tokar amon wuta daga dutsin Kelud a Indonesia REUTERS/Dwi Oblo
Talla

Dubban Mutane ne suka kauracewa gidajensu bayan dutsin na Kelud ya fara fitar da amon wuta.

Wannan ne kuma ya sa aka rufe Tasoshin jiragen sama a Shuraya da Solo da Yogyakarta saboda rashin ganin haske a dogon zango.

Tun lokacin da Dutsin zai fara fitar da amon wuta ne mahukuntan ƙasar suka bukaci ɗaruruwan mutanen da ke zama kusa da tsaunin su ƙaurace.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.