Indonesia
Mutane 22 sun mutu sakamakon Girgizan kasa a Indonesia
Hukumomin Kasar Indonesia sun ce girgizar kasar da aka samu a kasar, ya hallaka mutane 22, kuma sama da mutane 200 sun samu raunuka a Yammacin tsibirin Sumatra. Rahotanni sun ce, wasu yara shida sun mutu a cikin Masallacin Aceh, yayin da 14 kuma suka makale a ciki. Yanzu haka ana ci gaba da aikin ceto a kasar.
Wallafawa ranar: