Kotun ta bayar da umurnin kama jagoran zanga-zanga a Thailand
Kotun kasar Thailand ta bayar da umurnin kama shugaban masu zanga-zangar da ake gudanarwa a kasar bayan da dubban mutane suka mamaye muhimman cibiyoyin gwamnati da ke birnin Bangkok.
Wallafawa ranar:
Shugaban rundunar ‘yan sandar birnin, Kanar Sunthorn Kongklam, ya ce rundunarsa ce ta shigar da wannan bukata a gaban kotun hukunta masu aikata manyan laifufuka ta kasar, kuma tuni kotun ta bayar a umurnin cafke shugaban masu zanga-zangar.
Yau dai kwanaki 4 kenan bangarori biyu na siyasa da ke hamayya da juna ke zanga-zangar nuna goyon bayansu ga bangaren da suke marawa tsakanin gwamnati da kuma ‘yan adawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu