Dakarun Syria sun yi lugudan wuta a wasu yankunan ‘Yan tawayen
Dakarun kasar Syria sun yi lugudan wuta a wasu yankunan ‘Yan tawaye dake wajen birnin Damascus a wayewar garin yau Talata, a yayin da ake gwabzawa akan wake da iko kan garin Mastuma.
Wallafawa ranar:
Rahotanni na nuna cewa garuruwa da dakaarun suka kai hare-hare sun hada da garin Beit Saham da Maliha dake Kudu Maso Gabashin babban birnin na Damascus.
Har ila yau rahotannin na nuna cewa, an tura karin dakaru zuwa yankin domin su samu su kwato garin, wanda daruruwan mutane suka mutu a watan Agustan da ya gabata, kamar yadda kungiyar mai sa ido akan rikincin ta Observatory for Human Rights ta bayanna.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu