Isa ga babban shafi
Syria-MDD

Mutane 60,000 suka mutu a Syria, inji MDD

Kwamishinan hukumar kare Hakkin Bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya, Navi Pillay yace Akalla mutane 60,000 suka mutu a rikicin Syria da aka shafe shekaru Biyu ana yi tsakanin Gwamnati da masu adawa da Shugaba Bashar al Assad.

Wani Dan Jarida da ke aikon Dokar Hoto a rikicin Syria
Wani Dan Jarida da ke aikon Dokar Hoto a rikicin Syria Reuters/Handout
Talla

Majalisar Dinkin Duniyar ta fitar da wadannan alkalumman ne a dai dai lokacin da aka samu karin wasu mutum 12 da suka mutu sakamakon wani kazamin harin da aka kai a wani kauye kusa da birnin Damascus.

Navi Pillay ya bayyana wa babban taron Geneva cewar kamin watan Nuwamban bara, akalla mutune dubu Hamsin da Tara ne aka kashe a yakin da aka kwashe watanni 21 ana gwabzawa.

Rikicin Syria dai ya ya faro ne daga zanga-zangar kin jinin Gwamnatin Bashar Assad a watan Maris na shekarar 2011.

Sai dai majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewar yawan wadanda suka mutu a rikicin na Syria ya fi karfin hasashen su amma kuma abin ban tsoro ne.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.