MDD-Syria
Kofi Annan zai gana da Bashar Assad na Syria
Ana sa ran Kofi Annan, Jakadan Majalisar Dinkin Duniya na musamman a kasar Syria, zai gana da shugaba Bashar al assad, bayan kisan kiyashin da aka samu a Huola, wanda ya janyo suka daga sassan duniya. Bayan isar Annan Syria a jiya, Annan ya gana da Ministan harkokin wajen, Walid Muallem, da kuma shugaban tawagar masu sa ido, Janar Robert Mood inda ya bukaci gaggauta aje makamai.
Wallafawa ranar: