Isa ga babban shafi
Syria-MDD

Ban Ki-moon yace Al Qaeda ce ta kai hare hare a Syria

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki-moon yace Kungiyar Al-Qaeda ce ta kai wasu munanan hare haren bom a birnin Damascus a kasar Syria, wanda ya yi sanadiyar mutawar mutane da dama.

Harin Bom da aka kai a birnin Damascus na kasar Syria
Harin Bom da aka kai a birnin Damascus na kasar Syria Reuters
Talla

“Kwanaki da suka gabata, akwai harin bama bamai a Syria, kuma na yi imanin kungiyar al Qaeda ce ta kai hare haren. Wannan wata matsala ce da ta kunno kai.” Inji Ban Ki-moon a lokacin da yake ganawa da matasa a Hedikwatar Majalisar a Birnin New York.

Ban Ki-moon yace adadin wadanda suka mutu a Syria yanzu sun haura 10,000 tun fara zanga-zangar adawa da gwamnatin Bashar Al Assad.

Mista Ban yace Shugaba Bashar al-Assad ya ki fara aiwatar da shirin zaman lafiya ta Kofi Annan mai shiga tsakanin rikicin kasar.

A ranar 10 ga watan Mayu ne wasu ‘Yan kunar bakin wake suka tayar da bama bamai a birnin Damascus, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar a kalla mutane 55 da raunata kusan 400.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.