Isa ga babban shafi

An sace wasu Amurkawa 4 a Mexico

Mahukuntan Mexico da na Amurka suna aiki sau da kafa don tabbatar da ceto wasu Amurkawa 4 da wasu ‘yan bindiga suka yi awon gaba da su bayan da suka bude musu wuta a lokacin da suke ketarawa kan iyaka zuwa kasar.

Hukumar bincike ta FBI na neman Amurkawan da aka sace a iyakar Mexico.
Hukumar bincike ta FBI na neman Amurkawan da aka sace a iyakar Mexico. via REUTERS - SPANISH POLICE
Talla

Hukumar Binciken Manyan Laifuka ta FBI ta yi tayin bada dala dubu 50 ga duk wanda ya taimaka wajen gano wadanda aka yi  garkuwa da su, tare da kame masu garkuwar.

Ofishin Jakadancin Amurka a Mexico ya ce Amurkawan sun tsallaka garin Matamoros na jihar Tamaulipas ne a cikin wata karamar motar bas mai lambar North Carolina a ranar Juma’a.

Shugaban Mexico, Andres Manuel Lopez Obrador ya ce, rahotannin da ya samu na nuni da cewa wadannan Amurkawa sun shiga kasarsa ne don sayen magunguna, inda suka yi gamo da wadannan gungun masu aikata manyan laifuka.

Ya shaida wa manema labarai cewa mahukuntan Mexico na aiki tare da hukumar FBI ta Amurka don gano mutanen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.