Haɗarin mota ya kashe mutane 45 a Afirka ta Kudu
Ma'aikatar sufuri ta kasar Afirka ta Kudu ta tabbatar da mutuwar fasinjoji 45 cikin 46 da ke cikin wata motar Bus da ta fada wani kwazazzabo daga saman gada ta kuma kama da wuta.
Wallafawa ranar:
A cewar ministan sufurin kasar da ta kai ziyara inda iftila'in ya wakana ranar Alhamis, wata ƴarinya mai shekara takwas ne kadai ta tsira wanda aka yi gaggawar wuce wa da ita a asibiti.
Sanarwar da ma'aikatar ta fitar ta ce motar ta fito ne daga makociyar kasar Botswana ta kuma nufi garin Moria, wani gari da ke arewacin lardin limpopo da aka saba gudanar da bikin Easter, daga bisani motar ta kurce a hannun direban sannan ta fada a wani wuri mai tsaunuka dake yankin Mamatlakala mai nisan kilolita 300 daga arewacin birnin Johannesburg.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu