Isa ga babban shafi

Majalisar dokokin Togo ta fara muhawwara kan gyarar kundin tsarin mulkin kasar

Majalisar dokokin Togo ta fara mahawara a game da wani daftari da ke neman yi wa kundin tsarin mulkin kasar gyara, kuma matukar aka amince da gyarar, hakan zai sauya salo a game da yadda ake zaben shugaban kasa da kuma adadin shekarun da zai share kan karagar mulki.

Shugaban kasar Togo Faure Gnassingbé.
Shugaban kasar Togo Faure Gnassingbé. © Gnassingbe Twitter
Talla

Idan dai har majalisar ta amince da wannan sauyi, to hakan na nufin cewa Togo za ta daina amfani da tsarin shugaban kasa da da al’umma ke zabe kai-tsaye zuwa wanda ‘yan majalisar dokoki zabe.

Har ila yau daftarin ya ce za a zabi shugaban kasa domin yin wa’adin mulki na tsawon shekaru 7 har sau biyu, sabanin kundin tsarin mulkin da ake amfani da shi a yau da ake zaben shugaba tsawon shekaru 5 kacal.

Wani sauyi a cikin sabon daftarin shi ne, majalisa ce za ta rika nada firaminista da za a kira shi da suna shugaban gwamnati. Kundin tsari mulkin da kasar ke amfani da shi yanzu haka an kirkire shi ne tun 1992, to amma an yi masa gyare-gyare sau da dama, kuma na karshe shi ne wanda aka yi a 1999, kuma a karkashinsa, ana zaben shugaban kasa wa’adin shekaru 5 ne tare da damar sake tsayawa karo na biyu kawai.

To sai dai kungiyoyin da ke fafutuka domin tabbatar da dimokuradiyya a Togo, na ganin cewa ‘yan majalisar dokokin kasar ba su da hurumin zaunawa balantana yi wa kundin tsarin mulkin kasar gyara, domin kuwa wa’adin da aka zabe su a kai, ya kawo karshe tun a watan disambar da ya gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.