Isa ga babban shafi

Tawagogi 50 daga Afirka zasu halarci taron birnin Roma kan batun bakin haure

A yau ake soma taron birnin Roma na kasar Italiya da Afrika,tawagogi 50 daga kasashen Afirka zasu kasance a birnin na Roma. Shugabannin kasashen Turai da wakilan kungiyoyin kasa da kasa kuma za su halarci taron,inda gwamnatin Italiya ke shirin gabatar da sabon shirinta na dabaru wanda ke da nufin sake nazarin tsarin kasar game da nahiyar Afirka.

Wasu bakin haure a yankin Lampedusa na kasar Italiya
Wasu bakin haure a yankin Lampedusa na kasar Italiya © Cecilia Fabiano / AP
Talla

Italiya a wannan kokari na fatan ganin ta cimma daya daga cikin abubuwan da gwamnatin Giorgia Meloni ta sa gaba, wanda ya kamata ya mayar da ita a matsayin babban jigon kungiyar G7 da za ta shugabanta a watan Yuni mai zuwa.

Wasu daga cikin bakin haure zuwa Turai
Wasu daga cikin bakin haure zuwa Turai © Eric Gay / AP

Italiya na fafutukar ganin ta kafa kanta a matsayin mai iko a tekun Bahar Rum, musamman dangane da bakin haure.

Wani karamin jirgin ruwan masu yunkurin tsallakewa zuwa turai
Wani karamin jirgin ruwan masu yunkurin tsallakewa zuwa turai AFP - SAMEER AL-DOUMY

Daya daga cikin makasudin sabon shirin na gwamnati shi ne magance tushen tattalin arzikin da ke haifar da kwararar bakin haure daga Afirka zuwa Turai, tare da yawan bakin haure a Italiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.