Isa ga babban shafi

Mayakan RSF sun karkata hare-harensu zuwa sassan kudancin Sudan

An shiga wani yanayi na fargaba a sassan Sudan, bayan da mayakan RSF suka fara karfi a kudancin kasar, yankin da a baya rikicin na kusan watanni 8 bai kai gareshi ba, matakin da ke zuwa kwana guda bayan dakarun sojin kasar sun sanar da dakile hare-haren mayakan tare da fatattakarsu daga Wad Madani.

Taron mayakan RSF karkashin jagorancin Dagalo.
Taron mayakan RSF karkashin jagorancin Dagalo. AFP - -
Talla

A karshen makon jiye ne motocin mayakan RSF suka fara kutsa kai yankin na kudanci lamarin da ya sanya fargaba a zukatan al’ummar Al-Jazira musamman kauyukan da ke arewacin Wad Madani, fadar gwamnatin jihar mai dauke da ‘yan gudun hijira fiye da miliyan guda wadanda suka tserewa yakin kasar na kusan watanni 8 daga yankunansu.

Rabab wata mazauniyar yankin ta shaidawa AFP cewa yankin na shirin komawa dandalin yaki tsakanin mayakan na RSF da Sojin Sudan, bayan da ko a Asabar din da ta gabata mayakan suka kashe fararen hula akalla 8.

Wani ganau da shima ya nemi a sakaya sunansa saboda tsoron mayakan RSF wadanda suka yi kaurin suna wajen kisan fararen hula, ya shaidawa AFP cewa mayakan sun harbe mutanen ne lokacin da suka nemi dakatar da su daga satar kayakin jama’a.

Daga kudancin Khartoum kadai akwai fiye da fararen hula rabin miliyan da ke gudun hijira a Wad Madani bayan da yaki ya daidaita fadar gwamnatin kasar.     

Zuwa karshen watan Nuwamban da ya gabata, alkaluman mutanen da aka kashe a yakin na Sudan cikin watanni 8 ya kai mutum dubu 12 da 190 yayinda miliyoyi ke hijira a ciki da wajen kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.