Isa ga babban shafi

Dubban mutane sun tsere daga birnin Wad Madani na Sudan

Dubban mutanne ne suka yi ta arcewa daga birnin Wad Madani na kasar Sudan a jiya Asabar  sakamakon wani fada da ya  barke tsakanin dakarun kai daukin gaggawa na RSF da rundunar sojin kasar, lamarin da ya  bude wani sabon babi a rikicin da suka shafe watanni 8 suna gwabzawa.

Wasu mutane da ke kokarin barin Wad Madani.
Wasu mutane da ke kokarin barin Wad Madani. via REUTERS - ICRC
Talla

Hotunan bidiyo sun nuna dimbim mutane, akasari wadanda suka shiga birnin don neman mafaka  daga rikicin da ake yi a Khartoum su na kwashe kayansu su na barin birnin a kasa.

Rundunar sojin Sudan wadda ke rike da birnin tun da yakin ya barke a  Kharoum sun kaddamar da harin sama  kan dakarun RSF a gabashin brnin, a kokarin da suke na tura  su baya.

A watan Afrilu ne fada ya barke  tsakanin dakarun kai daukin gaggawa na  rundunar RSF da sojojin Sudan, lamarin da ya sanadin mutuwar dimbim mutane sakamakon ci gaba da ruruwada wutar rikicin ke yi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.