Isa ga babban shafi

Kungiyar kare 'Yan Jaridu ta (CPJ) ta yi kira da a sako 'yan jaridu a Togo

A kasar Togo, Kungiyar kare 'Yan Jaridu ta (CPJ) ta yi kira da a sako Loïc Lawson, darektan jaridar  Le Flambeau des Démocrates, da Anani Sossou, dan jarida mai rubutun ra'ayin ta hanyar yanar gizo, da ake  tsare  da su a gidan yarin Lome babban birnin kasar tun ranar  15 ga watan Nuwamban nan. 

Kungiyar kare 'Yan jaridu ta CPJ
Kungiyar kare 'Yan jaridu ta CPJ Reuters
Talla

‘Yan jaridan biyu dai na fuskantar tuhuma biyo bayan shigar da kara da Ministan tsare-tsare na Birane, Adedzé Kodjo ya yi kan zargin bata masa suna.  

Wadanan yan jarida a shafukan sada zumunta sun ambaci cewa, an sace kudin CFA miliyan 400 daga wani gida na wannan Minista. 

Wasu 'yan jarida a wani shigen bincike na yan Sanda
Wasu 'yan jarida a wani shigen bincike na yan Sanda © Reuters / Noel Kokou Tadegnon

Da gidan rediyo RFI ya tuntubi Jonathan Rozen, babban jami’in bincike a kungiyar kare ‘yan jarida (CPJ), ya yi la’akari da cewa Togo na bukatar sake duba dokokinta, domin a cewarsa aikin jarida ba laifi ba ne. 

"Halin da ake ciki yana da damuwa kuma ya cancanci kulawar mu, musamman tun da CPJ ta ba da kyautar 'yancin 'yan jarida ta kasa da kasa ga dan jaridar Togo Ferdinand Ayité.  

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.