Isa ga babban shafi

Kotun Gabon ta sallami Mike Jocktane da Thérence Gnembou

A Gabon, an saki wasu daga cikin yan adawa da suka hada da  Mike Jocktane da Thérence Gnembou ,da wani mutum da aka kama su tare a lokacin da suka yi kokarin neman shiga kasar Equatorial Guinea. 

Jagoran yan adawa a Gabon , Albert Ondo Ossa na kasar Gabon
Jagoran yan adawa a Gabon , Albert Ondo Ossa na kasar Gabon © Steeve Jordan / AFP
Talla

Kotun Gabon ta zartas da hukuncin sallamar wucin gadi a ranar Juma'a 13 ga Oktoba. Wadannan tsoffin 'yan takara a zaben shugaban kasa na baya-bayan nan da suka janye domin bayar da goyan baya  ga dan takarar adawa Albert Ondo Ossa.

Jama'a na goyon bayan sojojin da suka yi juyin mulki a Gabon
Jama'a na goyon bayan sojojin da suka yi juyin mulki a Gabon REUTERS - STRINGER

 

An cafke su a lokacin da suka yi kokarin isa kasar Equatorial Guinee da nufin  isar da sako ga shugabannin kasashe mambobin kungiyar kasashen tsakiyar Afrika.Jim kadan bayan kama su ne sojojin suka kiffar da Ali Bongo Ondimba,wanda hukumar zabe ta ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben kasar duk da cewa ba shida isasar lafiya. 

  

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.