Isa ga babban shafi

Harin 'yan ta'adda ya hallaka mutane 9 a arewacin Ghana

Wani harin kwanton bauna da ‘yan bindiga suka kai yayi sanadin mutuwar mutane 9 a yankin arewacin kasar Ghana.

Tuni rundunar sojin kasar ta aike da jami'ai da zasu tabbatar da zaman lafiya a yankin
Tuni rundunar sojin kasar ta aike da jami'ai da zasu tabbatar da zaman lafiya a yankin © AFP PHOTO / Etat Major des Armees
Talla

Guda daga cikin masu rike da sarautar gargajiya na yankin Pusiga da ke arewacin kasar Zubeiru Abdulai ya shaidawa manema labarai cewa harin ya faru ne a wani karamin kauye da ke dab da iyakar kasar da Burkina Faso, inda mayakan da ke ikirarin jihadi ke da karfi matuka.

Wani sojan kasar Burkina Faso yayin atasaye kan yaki da ta'addanci.
Wani sojan kasar Burkina Faso yayin atasaye kan yaki da ta'addanci. © REUTERS/LUCGNAGO

Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan ta’addar haye kan babura sun budewa wasu ‘yan kasuwa da ke hanyar su ta zuwa gurin sana’o’in su wuta nan take kuma 9 suka mutu sai wasu da dama da suka jikkata, wadanda yanzu haka ke karbar kulawar likitoci a babban asibitin Bawku.

Jami’an yan sandan yankin ta cikin wata sanarwa da suka fitar, sun ce mafi yawan wadanda lamarin ya rutsa da su mata ne.

Taswirar yankin Sahel mai fama da rikicin ta'addanci.
Taswirar yankin Sahel mai fama da rikicin ta'addanci. RFI

Ba’a cika samun rahoton ta’addanci a Ghana ba, sai dai ya zama tamkar ruwan dare a makwaftanta Burkina Faso, Togo da kuma Côte d'Ivoire, kasashen da mayakan da ke ta’addanci da sunan addini suka yi kakagida.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.