Isa ga babban shafi

An gano manyan kaburbura 13 a yankin Darfur - MDD

Ofishin kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya ce ya samu sahihan rahotannin gano wasu manyan kaburbura akalla 13 a garin El Geneina da ke yankin Darfur da kewayensa a Sudan.

Wasu mutane yayin ratsa kasuwar birnin El Geneina, babban birnin jihar Darfur ta Yamma a ranar 29 ga Afrilun 2023.
Wasu mutane yayin ratsa kasuwar birnin El Geneina, babban birnin jihar Darfur ta Yamma a ranar 29 ga Afrilun 2023. © AFP
Talla

Shugaban tawagar jami’an Majalisar Dinkin Duniya a kasar ta Sudan Volker Perthes ne ya bayyana haka, a lokacin da ya gabatar da jawabi kan halin da ake ciki a kasar ga kwamitin sulhu na Majalisar ta Dinkin Duniya.

Perthes ya ce manyan kaburburan da aka gano suna kunshe ne da wadanda aka kashe yayin hare-haren da dakarun rundunar RSF tare da kawancen wasu mayakan sa-kai larabawa ke kai wa farar hula, wadanda akasarinsu 'yan kabilar Masalit ne.

Jagoran  tawagar Majlisar Dinkin Duniyar ya kuma sanar da yin murabus daga mukaminsa a ranar Laraba, matakin da ake kyautata zaton na da alaka da gaza warware rikicin kasar ta Sudan a karkashin jagorancinsa.

Rikicin kabilanci a El Geneina, birnin da ke yammacin Darfur a kusa da kan iyaka da kasar Chadi, ya yi kamari tun bayan yaduwar kazamin rikicin da ya barke tsakanin dakarun RSF da suka bijire da sojojin Sudan a Khartoum babban birnin kasar, a tsakiyar watan Afrilu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.