Isa ga babban shafi

An yi harbe-harbe cikin dare a birnin Ouagadougou na Burkina Faso

Bayanai daga Burkina Faso na  cewa na jiyo karar harbe-harbe a tsakiyar birnin Ouagadougou gab da barikin sojin sama. 

Taswirar Burkina Faso.
Taswirar Burkina Faso. RFI
Talla

Kamfanin dillancin labaran Faransa AFP ya ruwaito cewa an fara jiyo harbin ne tun da misalin karfe 12:42 na tsakar daren jiya, abin da ake hasashen cewa ya yi kama da yunkurin juyin mulki. 

Wannan dai na zuwa ne bayan watanni 10 da juyin mulki kuma karo na biyu a kasa da shekara guda a kasar ta yammacin Africa mai fama da ayyukan ta’addanci. 

Har yanzu dai babu wani sahihin labari game da dalilin harbe-harben da ya taso daga gab da barikin sojoji. 

Idan mai saurare zai iya tunawa Kyaftin Ibrahim Traore ya hambarar da gwamnatin Kanal Paul-Henri Sandaogo Damiba, wanda shima kwace mulkin ya yi daga hannun Roch Marc Christian Kabore a watan Janairun 2022. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.