Isa ga babban shafi

'Yan Burkina Faso sun gudanar da gangamin neman sabon kundin tsarin mulki

Dubban mutane ne suka yi gangami a kan titunan birnin Ouagadougou  na Burkina Faso a ranar Asabar don nuna goyon baya ga sojojin da ke mulkin kasar daa rikicin ‘yan ta’adda masu ikirarin jihadi ya dabaibaye, inda suka mika bukatar sabon kundin tsarin mulki.

Masu zanga-zangar suna nuna goyon bayansu ga gwamnatin mulkin sojin kasar.
Masu zanga-zangar suna nuna goyon bayansu ga gwamnatin mulkin sojin kasar. AFP - OLYMPIA DE MAISMONT
Talla

Masu gangamin sun taru ne a tsakiyar babban  birnin na Burkina Faso, duk kuwa da ruwan sama mai kamar da bakin kwarya da aka yi.

Gamayyar kungiyoyin fararen hula ta kasar, wadda a karkashinta akwai sama da kungiyoyi 20 ce ta shirya wannan gangami.

Masu  zanga –zangar suna ta wakokin nuna goyon baya ga batun samar da sabon kundin tsarin mulki, tare da yin tir da abin da suka kira manufar Faransa ta bata wa Burkina Faso suna.

Suna ta daga tutocin Mali da Guinea, wato kasashe biyu, wadanda su ma sojoji ne ke jan ragamarsu.

Tun a shekarar 2015 ce Burkina Faso ke fama da matsalar kungiyoyin ‘yan ta’adda masu ikirarin jihadi, wadandaa suka kashe mutane da dama, tare da daidaita al’umma dayawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.