Isa ga babban shafi

‘Yan Sandan Brazil sun ceto wasu ‘yan Najeriya matafiya a gabar teku

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce an ceto wasu matafiya hudu a kudu maso gabashin gabar tekun Brazil bayan shafe kwanaki 13 a tekun.

Wani jirgin ruwa na  dako kaya
Wani jirgin ruwa na dako kaya © VIVEK PRAKASH/AFP
Talla

Mutanen sun boye ne a wani daki da ke wani bangare na jirgin dake kan hanyarsa na zuwa Brazil.

Ma’aikatan jirgin ruwan dake dauke da tutar kasar Laberiya ne suka same su, wanda ya taso daga Legas a ranar 27 ga watan Yuni.

Wani jirgi dauke da bakin haure saman teku
Wani jirgi dauke da bakin haure saman teku via REUTERS - GIACOMO ZORZI/SEA-WATCH

Wani jami'in 'yan sanda ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa AFP cewa mutanen hudun suna cikin koshin lafiya.

A cewar ‘yan sandan, ‘’yan sandan sun ceto mutanen da suka bayyana cewa su ‘yan Najeriya ne, amma ba su da wata takarda da ke tabbatar da asalinsu.

Sanarwar ta ce mutanen za su ci gaba da kasancewa a hannun Brazil har sai an mayar da su kasarsu ta asali.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.