Shugaba Raissi na Iran ya caccaki kasashen yammacin Duniya
Shugaban kasar Iran Ebrahim Raissi a ziyara da ya kai kasar Uganda ya bayyana damuwa ganin rawar da kasashen yammaci ke takawa a siyasar su da kasashen Afirka.
Wallafawa ranar:
Shugaban na Iran Ebrahim Raissi da zai kai ziyara a wasu kasashen Afirka da suka hada da Uganda da Zimbabwe da Kenya ya yaba da kokarin hukumomin kasar Uganda na haramta auren jinsi.
Kasar Ugnada a karkashin Shugabancin Yoweri Museveni ta aiwatar da dokoki na hukunta duk mutane dake ra’ayin auren jinsi tare da fuskantar dauri a gidan yari.
Shugaban na Iran ya bayyana goyan bayan sa ga hukumomin kasar ta Uganda,kasar Iran ta dau alkawalin taimakawa wajen gina matatar mai da kasar Uganda ta sanar a baya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu