Isa ga babban shafi

Gwamnatin Libya ta ce ba ta da hannu a harin da aka kai sansanin Wagner

Gwamnatin Libya mai samun goyon bayan kasashe ta   ce ba ta da hannu a harin jirgi mara matuki da aka kai wani sansanin dakarun sojin hayar Wagner a gabashin kasar.

Firaministan Libya Abdel Hamid Dbeibah.
Firaministan Libya Abdel Hamid Dbeibah. AP - Hazem Ahmed
Talla

Wata majiyar tsaro ta shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa a ranar Alhamis, wani jirgi mara matuki da ba a tantance asalinsa ba ya kai farmaki a sansanin sojin  saman al-Kharrouba mai nisan kilomita 150 daga kudu maso gabashin birnin Bengazi, inda aka yi amannar sansani ne na dakarun Wagner.

Wasu kafofin yada labarai na intanet sun danganta harin da sojin gwamnatin Libya da ke samun goyon bayan majalisar dinkin duniya, wadda abokiyar hamayyarta ta gabashin kasar ke ja da halarcinta.

Gwamnatin mai mazauni a birnin Tripoli ta bayyana mamakin a kan wannan rahoto, inda ta ce ba ta da hannu a ta’asar da Alhamis,  hasali ma tana  girmama yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma a watan Oktoban 2020.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.