Isa ga babban shafi

An yi luguden wuta a babban birnin Sudan duk da alkawarin tsagaita wuta don babbar Sallah

An yi ta kai hare hare ta sama tare da harba bindigogi masu kakkabe jiragen sama a birnin Khartoum na Sudan duk kuwa da tsagaita wuta da bangarorin da ke rikici da juna suka ayyana don bai wa Musulmi damar gudanar da shagulgulan babbar Sallah.

Hayaki ya turnike sararin sama a kudancin birnin Khartoum sakamakon wargajewar tsagaita wuta.
Hayaki ya turnike sararin sama a kudancin birnin Khartoum sakamakon wargajewar tsagaita wuta. © AFP
Talla

Yakin da ya barke tsakanin rundunar sojin Sudan da dakarun kai daukin gagawa na RSF a watan Afrilu ya yi sanadin babbar matsalar jinkai, kana ya daidaita kusan mutane miliyan 2 da dubu dari 8, inda daga cikin su akalla dubu  dari 6 da 50 suka tsallaka zuwa kasashen da ke makwaftaka da Sudan.

Birane 3 da ke gabar kogin Nilu a babbaan birninn kasar da suka hada da arewacin Khartoum da Omdurman sun shafe maakwani 10 cikin yanayi na mummunan rikici tsakanin baangarorin biyu da ke dauke da makamai, a yayin da ya haddasa sake bullar rikicin kabilanci.

Rahotanni sun ce an ci gaba da gwabza fada har a tsakar ranar Laraba a garin Omdurman.

 Zalika, kungiyar lauyoyi a yankin Darfur ta ce, dakarun RSF sun kai munanan hare-hare a yankin Manwashi na kudancin Darfur, karo na biyu a cikin kwanaki 5.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.