Harin ta'addanci ya kashe mutane 12 a Burkina Faso
Akalla Fararen hula 12 ne aka kashe yayin wani hari da wasu da ake zargin mayakan masu ikirarin jihadi ne suka kai a yammacin Burkina Faso.
Wallafawa ranar:
Majiyoyin tsaro da na cikin gida sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewar, tun daren Juma'a, wasu mutane dauke da makamai suka kai hari kauyen Sara da ke karamar hukumar Bekuy, kusa da Bobo-Dioulasso, birni na biyu mafi girma a kasar.
Shaidu suka ce, an binne gawarwakin mutane tara jiya Asabar, sai kuma wasu mutane biyu suka mutu daga bisani sakamakon raunukan da suka samu, abin da yakai adadin wadanda suka mutu zuwa goma sha daya.
Wani mazaunin garin ya ce ‘yan ta’addan sun shiga kauyen ne da misalin karfe 8:00 na dare agogon GMT.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu