Isa ga babban shafi

Taruwar 'yan tawayen SPLM-N Kordofan ya haifar da fargaba a kudancin Sudan

Bayanai daga wasu mazauna jihar Kordofan da ke Sudan, sun bayyana cewar mayakan ‘yan tawayen kungiyar SPLM-N masu yawan gaske na taruwa, lamarin da ya haifar da fargaba kan yiwuwar barkewar sabon rikici a yankunan kudancin kasar ta Sudan.

Hayaki da ke tashi a wasu sassan Khartoum babban birnin kasar Sudan yayin fafatawa tsakanin sojojin gwamnati da dakarun rundunar RSF da suka bijire.
Hayaki da ke tashi a wasu sassan Khartoum babban birnin kasar Sudan yayin fafatawa tsakanin sojojin gwamnati da dakarun rundunar RSF da suka bijire. REUTERS - MOHAMED NURELDIN ABDALLAH
Talla

Dakarun rundunar ta SPLM-N da aka kiyasta ta kunshi dubun dubatar mayaka dauke da muggan  makamai, na karkashin jagorancin babban kwamandansu Abdelaziz al-Hilu.

Har zuwa lokacin wannan wallafa, babu tabbas akan ko wane bangare Hilu zai marawa baya, a rikicin da ya barke tsakanin sojojin gwamnati da dakarun rundunar RSF a birnin Khartoum, ranar 15 ga watan Afrilu.

Rahotanni sun ce a cikin ‘yan watannin da suka gabata an yi artabu tsakanin mayakan ‘yan tawayen na SPLM-N da dakarun musamman na RSF, wadanda a yanzu suka bijirewa gwamnati.

A Khartoum babban birnin kasar ta Sudan kuwa, inda fada ya fi kamari, mazauna yankin sun ce har yanzu ana cigaba da gwabza fada da kuma kai hare-hare ta sama, musamman a ranar Alhamis, duk da sassaucin da aka samu a dalilin yarjejeniyar tsagaita wutar da ta ba da damar kai wa fararen hula agajin gaggawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.