Sojojin Majalisar Dinkin Duniya 7 sun jikkata a Mali
Majalisar Dinkin Duniya ta ce dakarunta na wanzar da zaman lafiya 7 ne suka samu raunuka a tsakiyar kasar Mali ranar Asabar bayan da wani bam da aka dana a gefen hanya ya tashi a karkashin ayarin motocinsu.
Wallafawa ranar:
Cikin sanarwa da rundunar MINUSMA ta fitar ta shafukan sada zumunta yanzu haka sojojin na samun kulawa a wani asibiti ba tare da karin bayani kan yanayin da suke ciki ba ko kasar da suka fito.
Bam din ya tashi ne a lokacin da ayarin motocin ke kan hayarsa ta zuwa kauyn Douentza dake arewacin kasar.
Rundunar ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce an kai makamaita hare-hare kan dakarunta har sau shida a cikin wannan shekara a tsakiyar Mail, dake fama da kungiyoyi masu ikirarin jihadi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu