Isa ga babban shafi

Wakilan sojin Sudan sun isa Saudiyya don tattaunawar tsagaita wuta

Rundunar sojin Sudan ta aike da tawagar da za ta wakilce ta a birnin Jeddah na Saudiyya don tattaunawar tsagaita wuta, wanda Amurka da Saudiyya suka shirya.

Shugaban gwamnatin sojin Sudan,Abdelfattah Al-Burhan  da shugaban rundunar kai daukin gaggawa  Mohamed Hamdan Dogolo, dit "Hemedti" ; commandant des Forces de soutien rapide
Shugaban gwamnatin sojin Sudan,Abdelfattah Al-Burhan da shugaban rundunar kai daukin gaggawa Mohamed Hamdan Dogolo, dit "Hemedti" ; commandant des Forces de soutien rapide © Ashraf Shazly - AFP
Talla

Bayanin haka ya fito ne a wata sanarwar da sojin Sudan din ta fitar a daren Juma’a.

A yammacin Juma’a ne tawagar ta baro Sudan Zuwa birnin Jeddah, a yayin da sojin da ma abokan hammayarsu na RSF suka ce za su tattauna tsagaita wuta ce kawai bisa dalilai na jinkai amma ba don kawo karshen rikicin kacokan ba.

Gwamnatocin Amurka da Saudiyya sun tabbatar da cewa za a fara tattaunawa kai tsaye a tsakanin sojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na musamman a ranar Asabar din nan.

A wata sanarwa, Amurka da Saudiyya sun bukaci dukkan bangarorin da ke rikici da juna su yi la’akari da kasarsu da jama’arsu a yayin  tattaunawar tsagaita wutar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.