An kashe wani matashi a zanga-zangar kasar Kenya
‘Yan sanda sun yi amfani da ruwn zafi da kuma barkonon tsohuwa wajen tarwatsa zanga-zangar da madugun ‘yan adawa ya shirya a kasar Kenya, game da tsadar rayuwa.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:31
A cewar AFP, an kashe wani matashi a Kisumu da ke yammacin kasar, wato yankin da Raila Odinga ke da karfin magoya baya.
An tsaurara matakan tsaro a Nairobi, babban birnin kasar fiye da makon da ya wuce, da nufin haramta wa magoya bayan jagoran ‘yan adawa taruwa.
Shiga alamar sauti, domin sauraron rahoton George Ajowi na sashen Kiswahili daga Nairobi, wanda Shamsiyya Haruna ta fassara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu