Isa ga babban shafi

An sanya dokar takaita zirga zirga a Burkina Faso don yaki da ta'addanci

Mahukuntan Burkina Faso sun kakaba  dokar takaita zirga zirga a tsakiyar yankin gabashin kasar da zummar taimakawa wajen yaki da ta’addanci, kamar yadda wani kundi da kamfanin dillancin labaran Faransa ya gani  a wannan Lahadin ya nuna.

Taswirar  Burkina Faso.
Taswirar Burkina Faso. © Studio FMM
Talla

Matsalar ta’addanci da aka shafe shekaru da dama ana kokarin dakilewa ta yi sanadin mutuwar dubban fararen hula, ‘yan sanda da sojoji, kana ta tilasta wa sama da mutaane miliyan 2 rabuwa da muhallansu.

Umurnin da ya fito daga ofishin gwamnan yankin gabashin kasar, Kouilga Abert Zongo  ya nuna cewa za a takaita zirga zirgar mutane da ababen hawa daga daga karfe 10 na dare zuwa karfe 5 na asuba. 

Zongo ya ce wannan dokar takaita zirga zirga za ta taimaka wa dakarun da ke yaki da ta’addancin a kan iyakar kasar da Mali, inda matsalar ta kunno kai tun a shekarar 2015.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.