Isa ga babban shafi

'Yan ta'adda sun kashe sama da fararen hula 10 a Burkina Faso

Mutane sama da 10 ne suka mutu a sakamakon wasu jerin hare-haren da mayakan ta’addanci suka kai musu a yankin Dassa a cewar mahukuntan kasar.

'Yan ta'adda ssun afka wa sun kashe sama da mutane 10 kusa da babban birnin Burkina Faso Ouagadougou.
'Yan ta'adda ssun afka wa sun kashe sama da mutane 10 kusa da babban birnin Burkina Faso Ouagadougou. © RFI
Talla

Bayanai sun ce maharan su kaddamar da harin ne kan fararen hula a garin da ke da nisan kilomita 140 daga babban birnin kasar Ougadougou, inda kuma suka hallaka mutane 12 nan take.

Burkina faso dai na cikin kasashen Sahara dake fama da ayyukan ta’addanci, da ya raba dubban fararen hula da jami’an tsaro da rayukan su, sai miliyoyin da suka zama ‘yan gudun hijira bayan guduwa don tsira da rayukan su.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.