Isa ga babban shafi

Harin kunar bakin wake na Al-Shabaab ya kashe mutane 7 a Somalia

Rundunar sojojin Somalia da kuma shaidun gani da ido, sun ce wani harin kunar bakin wake da kungiyar Al-Shabaab ta dauki alhakin kai wa a Mogadishu babban birnin kasar, ya kashe akalla mutane bakwai tare da jikkata wasu a jiya Lahadi.

Mayakan Al-Shabaab na kasar Somalia
Mayakan Al-Shabaab na kasar Somalia RFI-Swahili
Talla

Daya daga cikin kwamandojojin Sojan Somalia Abdul Adnan, ya ce wani dan ta’adda ne ya tarwatsa kansa da safiyar jiya Lahadi a kusa inda ake daukar sabbin kuratan sojoji a wani sansanin soja da ke kudancin birnin Mogadishu.

A farkon watan nan ne dai, mayakan Al Shebaab suka kashe fararen hula akalla 19, yayin wani hari da suka kai a yankin tsakiyar kasar.

A watan Agusta, kungiyar Al-Shabab din ta kaddamar da wani gagarumin hari a wani otel a birnin Mogadishu, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 21 tare da jikkata 117.

Shugaban Somalia, Hassan Sheikh Mohamud yana fuskantar sake bayyanar kungiyar Al-Shabaab tun bayan da aka zabe shi a watan Mayu, kuma ya sha alwashin yin fito na fito da ita da zumar murkushe ta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.