Isa ga babban shafi

Barayin shannu sun kashe kauyawa 32 a wani kauyen Madagascar

A Madagascar, akalla kauyawa 32  ne suka kone kurmus inda ake kyautata zaton barayin shannu a lardin Ankazobe suka tilasta musu shiga dakunan su ,daga bisani suka cinawa gidajen wuta.

Taswirar kasar Madagascar
Taswirar kasar Madagascar © RFI
Talla

Masu kai dauki sun samu nasar ceto mutane uku daga cikin  wutar, yayin da hukumomi suka kaddamar da bincike da nufin tattance barayin da suka aikata wannan barna a kauyen na Ankazobe.

 Gwamnatin kasar ta tura da karin sojoji da yan sanda zuwa wannan yanki, al’amarin da gwamnati ta bayyana shi a matsayin bakin labari.

Wasu daga cikin yankunan kasar ta Madagascar sun kasance masu tattare da hatsari inda ake yawaitar hare-haren barayin shannu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.