Isa ga babban shafi

Belgium ta mayar da hakorin Lumumba ga iyalansa

Kasar Belgium ta mika hakorin tsohon shugaban Jamhuriyar Demokradiyar Congo Patrice Lumumba, wanda 'yan aware da sojojin haya na Belgium suka kashe, mutumin da ya yi shura wajen yaki da mulkin mallaka.

Hakurin tsohon shugaban kasar Jamhuriyar Demokradiyar Congo Patrice Lumumba cikin akwatin gawa a Brussel, 20/06/22.
Hakurin tsohon shugaban kasar Jamhuriyar Demokradiyar Congo Patrice Lumumba cikin akwatin gawa a Brussel, 20/06/22. © RFI/Paulina Zidi
Talla

Kisan Lumumba da kuma mummunan tarihin da Belgium ta yi a Demokradiyar Comngo ya kasance mai daure kai a tsakanin kasashen biyu.

An sanya hakorin a cikin wani akwati da aka lullube da wani kyalle mai launin tutar Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, domin karrama Lumumba.

Lumumba mai sukar salon mulkin Belgium, ya zama firaministan kasarsa na farko bayan samun 'yancin kai a shekarar 1960.

Kisan Lumumba

An kashe shi a ranar 17 ga Janairun 1961, yana da shekaru 35, a yankin kudancin Katanga, bisa goyon bayan sojojin haya na Belgium, inda aka narkar da gawarsa da sinadari mai guba.

Tsohon shugaban kasar Congo Patrice Lumumba a shekarar 1960.
Tsohon shugaban kasar Congo Patrice Lumumba a shekarar 1960. AP - Horst Faas

Amma daya daga cikin wadanda suka kashe shin, dan kasar Belgium ya ajiye hakorin a matsayin tarihi.

Har yanzu dai ana ci gaba da gudanar da bincike kan laifukan yaki amma biyu daga cikin jami'an da suka kashe shi suna raye.

Kisan mutane da dama

Masana tarihi sun ce miliyoyin mutane ne aka kashe, ko aka batar da su ko kuma suka mutu sakamakon kamuwa da cutar, yayin da aka tilasta musu tara roba a karkashin mulkin Belgium. Haka kuma an mamaye kasar ne saboda arzikin ma'adinai, katako da hauren giwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.